15 Firist kuwa zai ɗibi man, ya zuba shi a tafin hannunsa na hagu.
16 Ya kuma tsoma yatsan hannunsa na dama a cikin man da yake a tafin hannunsa na hagu, ya yayyafa man da yatsansa sau bakwai a gaban Ubangiji.
17 Sauran man da ya ragu a tafin hannunsa, sai ya shafa shi a leɓatun kunnen dama na wanda za a tsarkake, da bisa babban yatsan hannunsa na dama, da na ƙafar dama. Wato, za a shafa man a inda aka shafa jinin hadaya don laifin.
18 Sauran man kuma da ya ragu cikin tafin hannunsa, firist ɗin zai shafa a kan wanda za a tsarkake. Firist zai yi kafara dominsa gaban Ubangiji.
19 Sai firist ya miƙa hadaya don zunubi domin ya yi kafara, don rashin tsarkin mutumin. Daga baya ya yanka hadaya ta ƙonawa.
20 Firist kuma zai miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta gari a bisa bagaden. Da haka zai yi kafara dominsa, shi kuwa zai tsarkaka.
21 Amma idan matalauci ne, har ba zai iya samun waɗannan abubuwa ba, sai ya kawo ɗan rago ɗaya domin hadaya don laifi, a yi hadaya ta kaɗawa, a yi kafara dominsa. Ya kuma kawo humushin garwa na gari mai laushi kwaɓaɓɓe da man zaitun don yin hadaya ta gari, da rabin moɗa na mai,