1 Ubangiji kuma ya ce wa Musa,
2 “Ka ƙera kakaki biyu na azurfa don ka riƙa kirawo taron jama'a, don kuma ka riƙa sanashe su lokacin tashi daga zangon.
3 Lokacin da aka busa kakaki biyu ɗin gaba ɗaya, sai taron jama'a duka su tattaru a wurinka a ƙofar alfarwa ta sujada.
4 Amma idan ɗaya kaɗai aka busa, sai shugabannin Isra'ila su tattaru a wurinka.
5 Sa'ad da kuka yi busar faɗakarwa, waɗanda suke zaune a gabashin zangon za su tashi.
6 Sa'ad da kuma kuka yi busar faɗakarwa ta biyu, waɗanda suke a kudancin zangon za su tashi. Sai a yi busar faɗakarwa a kowane lokaci da za su tashi.