20 Sai Ubangiji ya ce, “Saboda maganarka na gafarta.
21 Amma, hakika, na rantse da zatina, kamar yadda ɗaukakata za ta cika duniya duka,
22 dukan mutanen da suka ga ɗaukakata da alamuna waɗanda na aikata a Masar, da kuma a jejin, suka kuwa jarraba ni har sau goma, ba su kuma yi biyayya da maganata ba,
23 ba za su ga ƙasar da na rantse zan ba kakanninsu ba. Duk waɗanda suka raina ni, ba za su ga ƙasar ba,
24 sai dai bawana Kalibu da yake ruhunsa dabam ne, gama ya bi ni sosai.
25 Yanzu fa, tun da yake Amalekawa da Kan'aniyawa suna zaune a kwarin, gobe sai ku juya ku nufi wajen jejin ta hanyar Bahar Maliya.”
26 Ubangiji kuma ya ce wa Musa da Haruna,