47 Sai Haruna ya ɗauko farantin turaren, ya yi yadda Musa ya ce. Ya sheƙa a guje a tsakiyar taron jama'a. Amma an riga an fara annobar a cikin jama'a. Sai ya zuba turare, ya yi kafara domin jama'a.
48 Ya kuwa tsaya a tsakanin matattu da masu rai, annobar kuwa ta tsaya.
49 Waɗanda annoba ta kashe mutum dubu goma sha huɗu ne da ɗari bakwai (14,700), banda waɗanda suka mutu a sanadin Kora.
50 Sai Haruna ya koma wurin Musa a ƙofar alfarwa ta sujada, gama annobar ta ƙare.