15 Kabilan nan biyu da rabi sun karɓi nasu gādo a wancan hayin Urdun a gabashin Yariko.”
16 Ubangiji kuma ya ce wa Musa,
17 “Ga sunayen mutanen da za su taimake ka raba gādon ƙasar, Ele'azara firist, da Joshuwa ɗan Nun.
18 Za ka kuma ɗauki shugaba ɗaya daga kowace kabila don su raba gādon ƙasar.
19 Waɗannan su ne sunayen mutanen, Kalibu ɗan Yefunne daga kabilar Yahuza.
20 Shemuyel ɗan Ammihud daga kabilar Saminu.
21 Elidad ɗan Kislon daga kabilar Biliyaminu.