24 “Ubangiji ya sa muku albarka, ya kiyaye ku.
25 “Ubangiji ya sa fuskarsa ta haskaka ku, ya yi muku alheri.
26 “Ubangiji ya dube ku da idon rahama, ya ba ku salama.”
27 Idan suka sa wa jama'a wannan albarka sa'ad da suke addu'a ga Ubangiji domin Isra'ilawa, Ubangiji zai sa musu albarka.