27 Ya fāɗi a gwiwoyinta,Ya fāɗi ƙasa, yana kwance shiru a ƙafafunta.A ƙafafunta ya sunkuya ya fāɗi,Ya fāɗi matacce har ƙasa.
28 Mahaifiyar Sisera ta duba ta tagogi,Ta leƙa ta kariyar taga, ta ce,“Me ya sa karusarsa ta yi jinkirin zuwa?Don me dawakansa ba su komo da wuri ba?”
29 'Yan matanta mafi hikima suka amsa mata,Ita kuwa ta yi nanatawa, tana cewa,
30 “Nema suke kurum su sami ganima, su raba,Yarinya ɗaya ko biyu domin kowane soja,Tufafi masu tsada domin Sisera,Rinannun tufafi masu ado domin sarauniya.”
31 Ta haka, ya Ubangiji ka sa maƙiyanka su mutu,Amma abokanka su haskaka kamar fitowar rana!Ƙasar kuwa ta zauna lafiya shekara arba'in.