12 Haka nan kuma a dā Horiyawa ne suke zaune a ƙasar Seyir, amma mutanen zuriyar Isuwa suka zo, suka kore su, suka karkashe su, suka zauna a wurin, daidai kamar yadda Isra'ilawa suka yi da ƙasar mallakarsu, wadda Ubangiji ya ba su.)
13 “ ‘Yanzu, ku tashi ku haye rafin Zered da kanku.’ Sai kuwa muka haye.
14 Lokacin da muka tashi daga Kadesh-barneya zuwa lokacin da muka haye rafin Zered, shekara talatin da takwas ne. Duk wannan lokaci dukan waɗanda suka isa yaƙi suka murmutu kamar yadda Ubangiji ya rantse a kansu.
15 Hakika kuwa ikon Ubangiji ya buge su har suka hallaka ƙaƙaf.
16 “Sa'ad da dukan waɗanda suka isa yaƙi suka mutu,
17 sai Ubangiji ya yi mini magana, ya ce,
18 ‘Yau za ku ratsa kan iyakar ƙasar Mowab a Ar.