4 domin ba su zo sun tarye ku, su kawo muku abinci da ruwa ba sa'ad da kuke a hanyarku, lokacin da kuka fito daga Masar. Ga shi kuma, sun yi ijara da Bal'amu ɗan Beyor daga Fetor ta Mesofatamiya ya zo ya la'anta ku.
5 Amma Ubangiji Allahnku ya ƙi saurarar Bal'amu, sai Ubangiji ya juyar da la'anar ta zama muku albarka saboda Ubangiji Allahnku yana ƙaunarku.
6 Har abada kada ku nemar musu zaman lafiya ko wadata.
7 “Kada ku ji ƙyamar Ba'edome gama shi danginku ne. Kada kuma ku ji ƙyamar Bamasare don kun yi baƙunci a ƙasarsa.
8 'Ya'yansu tsara ta uku, za su iya shiga taron jama'ar Ubangiji.”
9 “Sa'ad da kuka kafa sansani don ku yi yaƙi da magabtanku, sai ku kiyaye kanku daga kowane mugun abu.
10 Idan wani a cikinku ya ƙazantu saboda ya zubar da maniyyi da dare, to, sai ya fita daga sansanin, kada ya koma sansanin.