15 “Yeshurun ya yi ƙiba, yana harbin iska,Ka yi ƙiba, ka yi kauri, ka yi sumul.Ya rabu da Allahn da ya yi shi,Ya raina Dutsen Cetonsa.
16 Suka sa shi kishi, saboda gumaka,Suka tsokani fushinsa da abubuwan banƙyama.
17 Suka miƙa hadayu ga aljannun da ba Allah ba,Ga gumakan da ba su sani ba,Sababbin allolin da aka shigo da su daga baya,Waɗanda kakanninku ba su ji tsoronsu ba.
18 Kun ƙi kula da Dutsen da ya haife ku,Kun manta da Allahn da ya ba ku rai.
19 “Ubangiji ya gani, ya raina su,Saboda tsokanar da 'ya'yansa mata da maza suka yi masa.
20 Ya ce, ‘Zan ɓoye musu fuskata,Zan ga yadda ƙarshensu zai zama.Gama su muguwar tsara ce,'Ya'ya ne marasa aminci.
21 Suka sa ni kishi da abin da ba Allah ba,Suka tsokani fushina da gumakansu,Ni kuma zan sa su su yi kishi da waɗanda suke ba mutane ba.Zan tsokane su da wawanyar al'umma.