22 A kan Dan, ya ce,“Dan ɗan zaki ne,Mai tsalle daga Bashan.”
23 A kan Naftali, ya ce,“Ya Naftali, ƙosasshe kake da alheri,Cike kake da albarkar Ubangiji.Sai ka mallaki tafki da wajen kudu.”
24 A kan Ashiru, ya ce,“Ashiru mai albarka ne fiye da sauran 'yan'uwansa,Bari ya zama abin ƙauna ga 'yan'uwansa,Ya kuma tsoma ƙafarsa cikin mai.
25 Kurfanka na baƙin ƙarfe ne da tagulla,Ƙarfinka ba zai rabu da kai ba muddin ranka.”
26 “Babu wani kamar Allahn Yeshurun,Wanda yakan sauko daga Sama don ya cece ka,Wanda ya sauko daga bisa da ɗaukakarsa.
27 Allah Madawwami, shi ne wurin zamanka,Madawwaman damatsansa suna tallafarka,Yana kore maka maƙiyanka,Ya ce, ‘Ka hallaka su!’
28 Da haka Isra'ila yana zaune lafiya,Zuriyar Yakubu tana zaune ita kaɗaiA ƙasa mai hatsi da ruwan inabi,Wurin da raɓa take zubowa daga sama.