5 Zan zama kamar raɓa ga Isra'ila,Isra'ila za ta yi fure kamar lili,Saiwarta za ta shiga kamar itacen al'ul.
6 Tohonta zai buɗo,Kyanta zai zama kamar itacen zaitun,Ƙashinta kuwa kamar itacen al'ul na Lebanon.
7 Waɗanda za su komo, za su zauna a inuwarta,Za su yi noman hatsi da yawa.Za su yi fure kamar kurangar inabi.Ƙanshinsu zai zama kamar ruwan inabi na Lebanon.
8 Ya mutanen Ifraimu, me zan yi da gumaka?Ni ne wanda yake amsa muku, mai lura da ku kuma.Ni kamar itacen fir ne mai ganyaye kore shar.Daga gare ni, kuke samun 'ya'ya.”
9 Duk wanda yake da hikima, bari ya fahimci abubuwan nan.Duk wanda yake da ganewa, bari ya san abubuwan nan,Gama hanyoyin Ubangiji masu gaskiya ne,Masu adalci kuwa za su yi tafiya a cikinsu,Amma masu zunubi za su yi tuntuɓe a kansu.