8 Saboda haka, bala'inta zai aukar mata rana ɗaya,Mutuwa, da baƙin ciki, da yunwa.Za a kuma ƙone ta,Domin Ubangiji Allah da yake hukunta ta Mai Ƙarfi ne.”
9 Sarakunan duniya kuma da suka yi fasikanci da zaman almubazzaranci da ita, za su yi mata kuka da kururuwa, in sun ga hayaƙin ƙunarta,
10 za su tsaya a can nesa, don tsoron azabarta, su ce,“Kaitonka! Kaitonka, ya kai babban birni!Ya kai birni mai ƙarfi, Babila!A sa'a ɗaya hukuncinka ya auko.”
11 Attajiran duniya kuma suna yi mata kuka suna baƙin ciki, tun da yake, ba mai ƙara sayen kayansu,
12 wato, zinariya, da azurfa, da duwatsun alfarma, da lu'ulu'u, da lallausan lilin, da hajja mai ruwan jar garura, da siliki, da jan alharini, da itacen ƙanshi iri iri, da kayan hauren giwa iri iri, da kayan da aka sassaƙa da itace mai tsada, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na dutse mai sheƙi,
13 da kirfa, da kayan yaji, da turaren wuta, da mur, da lubban, da ruwan inabi, da mai, da garin alkama, da alkama, da shanu, da tumaki, da dawaki, da kekunan doki, da kuma bayi, wato, rayukan 'yan adam.
14 “Amfanin da kika ƙwallafa rai a kai, har ya kuɓuce miki,Kayan annashuwarki da na adonki sun ɓace miki, ba kuwa za a ƙara samunsu ba har abada!”