17 Da Dawuda ya ga mala'ika wanda yake hallakar da mutanen, sai ya ce wa Ubangiji, “Na yi laifi, na aikata mugunta, amma me waɗannan tumaki suka yi? Ina roƙonka, ka hukunta ni da gidan ubana.”
18 A ran nan Gad ya koma wurin Dawuda ya ce masa, “Ka haura ka gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna Bayebuse.”
19 Dawuda kuwa ya haura bisa ga umarnin Ubangiji ta bakin Gad.
20 Da Arauna ya waiga, ya ga sarki da fādawansa suna zuwa wurinsa, sai ya tafi ya tarye su. Ya tafi ya rusuna a gaban sarki har ƙasa,
21 ya ce, “Ranka ya daɗe, ya sarki, me ya kawo ka?”Sai Dawuda ya ce, “Don in sayi masussukarka ne domin in gina wa Ubangiji bagade, domin a kawar wa mutanen da annobar.”
22 Arauna kuwa ya ce wa Dawuda, “Bari ubangijina, sarki, ya karɓa, ya yi abin da yake so. Ga shanun nan domin hadayar ƙonawa, ga kuma itacen sussuka da karkiya domin itacen hadayar.”
23 Dukan waɗannan Arauna ya ba sarki. Ya kuma ce wa sarki, “Ubangiji Allahnka ya karɓa.”