32 Suka binne Abner a Hebron. Sarki ya ta da murya ya yi kuka a kabarin Abner. Dukan mutane kuma suka yi kuka.
33 Sarki ya yi wannan makoki domin Abner, ya ce,“Don me Abner zai mutu kamar wawa?
34 Hannuwansa ba a ɗaure suke ba,Ƙafafunsa kuma ba a dabaibaye suke ba.Ya mutu kamar wanda mugayen mutane suka kashe.”Dukan mutane suka yi kuka kuma saboda shi.
35 Mutane kuwa suka zo su ba Dawuda magana, ko ya ci abinci tun rana ba ta faɗi ba. Amma Dawuda ya rantse ya ce, “Allah ya buge ni in mutu nan, idan na ɗanɗana abinci ko wani abu kafin rana ta faɗi.”
36 Da mutanen suka lura, sai suka yarda da abin da sarki ya yi, suka kuma ji daɗin kowane abu da sarki ya yi.
37 A wannan rana dukan mutanen Dawuda da dukan mutanen Isra'ila suka gane, ashe, ba nufin Dawuda ba ne a kashe Abner ɗan Ner.
38 Sarki ya ce wa fādawansa, “Ba ku sani ba, basarake ne, babban mutum ne kuma ya faɗi a cikin Isra'ila yau?