23 Amma a gare su dūbān nan ba gaskiya ba ce, gama sun riga sun yi rantsuwa mai nauyi, amma zai tuna musu da laifinsu, don a kama su.
24 Domin haka ni Ubangiji Allah na ce, tun da yake kun sa a tuna da laifofinku, an kuma tone su, laifofinku kuma sun bayyana cikin ayyukanku, kun tonu, to, za a kama ku a cikinsu.
25 “Kai kuma ƙazantaccen mugu, yariman Isra'ila, ranarka ta zo, lokacin hukuncinka ya yi.
26 Ni Ubangiji Allah na ce, ka cire rawaninka, ka ɗauke kambinka. Abubuwa ba za su kasance kamar yadda suke a dā ba. Za a ɗaukaka ƙasƙantacce, amma a ƙasƙantar da maigirma.
27 Halaka, halaka, zan hallakar, ba za a bar ko alama ba, sai mai shi ya zo, shi ne zan ba shi.”
28 “Kai ɗan mutum, ka yi annabci, ka ce, ga abin da Ubangiji Allah ya ce a kan Ammonawa, da a kan zarginsu.‘An zare takobi don kashe-kashe,An goge shi don ya yi sheƙi kamar walƙiya!
29 Ka faɗa wa Ammonawa, cewa wahayin da suke gani ƙarya ne annabcin da suke yi kuma ƙarya ne. Su mugaye ne, ranar hukuncinsu tana zuwa. Za a sare wuyansu da takobi.