5 “Saminu da Lawi 'yan'uwa ne,Suka mori takubansu cikin ta dahankali.
6 Ba zan shiga shawararsu ta asiri ba,Ba kuwa zan sa hannu cikin taronsuba,Gama cikin fushinsu suka kashemutane,Cikin gangancinsu kuma sukagurgunta bijimai.
7 La'ananne ne fushinsu domin maitsanani ne,Da hasalarsu kuma, gama bala'i ce.Zan warwatsa su cikin dukan ƙasarYakubu,In ɗaiɗaitar su su cikin Isra'ilawa.
8 “Yahuza, 'yan'uwanka za su yabeka,Za ka shaƙe wuyan maƙiyanka,'Yan'uwanka za su rusuna agabanka.
9 Yahuza ɗan zaki ne,Ya kashe ganima sa'an nan ya komowurin ɓuyarsa.Yahuza kamar zaki yake,Yakan kwanta a miƙe,Ba mai ƙarfin halin da zai tsokaneshi.
10 Yana riƙe da sandan mulkinsa,Ya sa shi a tsakanin ƙafafunsa,Har Shilo ya zo.Zai mallaki dukan jama'o'i.
11 Zai ɗaure aholakinsa a kurangarinabi,A kuranga mafi kyau,Zai wanke tufafinsa da ruwan inabi,Ruwan inabi ja wur kamar jini.