1 Zan tsaya a wurin tsayawata,In zauna kuma a kan hasumiya,In jira in ji abin da zai ce mini,Da abin da zai amsa a kan kukata.
2 Sai Ubangiji ya ce mini,“Ka rubuta wahayin da kyau a kan alluna,Yadda kowa zai karanta shi a sawwaƙe.
3 Gama har yanzu wahayin yana jiran lokacinsa,Yana gaggautawa zuwa cikarsa,Ba zai zama ƙarya ba.Ka jira shi, ko da ka ga kamar yana jinkiri,Hakika zai zo, ba zai makara ba.
4 Wanda zuciyarsa ba daidai take ba, zai fāɗi,Amma adali zai rayu bisa ga bangaskiyarsa.
5 “Ruwan inabi kuma yana yaudarar mai fariya,Don haka ba ya zama a gida.Haɗamarsa tana da fāɗi kamar Lahira,Kamar kuma mutuwa yake, ba ya ƙoshi.Ya tattara wa kansa al'ummai duka,Ya kwaso wa kansa mutane duka.”
6 “Ai, waɗannan duka za su yi ta yi masa zambo,Su yi masa dariya ta raini,Su ce, ‘Tasa ta ƙare, shi wanda ya tattara abin da ba nasa ba,Har yaushe zai riƙa arzuta kansa ta hanyar ba da rance?’