18 Gama haka Ubangiji ya ce,“Ga shi, ina jefar da mazaunanƙasar daga ƙasarsu a wannanlokaci,Zan kawo musu wahala, za su kuwaji jiki.”
19 Tawa ta ƙare, saboda raunin da akayi mini.Raunina mai tsanani ne,Amma na ce, lalle wannan azaba ce,Tilas in daure da ita.
20 An lalatar da alfarwata,Dukan igiyoyi sun tsintsinke,'Ya'yana maza sun bar ni, ba sunan.Ba wanda zai kafa mini alfarwataYa kuma rataya labulena.
21 Makiyayan dakikai ne,Ba su roƙi Ubangiji ba,Don haka ba su sami wadata ba,An watsa dukan garkensu.
22 Ku ji fa, an ji ƙishin-ƙishin! Ga shikuma, yana tafe.Akwai babban hargitsin da ya fitodaga arewa,Don a mai da biranen Yahuza kufai,wurin zaman diloli.
23 “Ya Ubangiji, na sani al'amuranmutum ba a hannunsa suke ba,Ba mutum ne yake kiyaye takawarsaba
24 Ka tsauta mini, ya Ubangiji, ammada adalcinka,Ba da fushinka ba, don kada kawofinta ni.