1 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, ya ce, “Tafi ka sayo lilin na yin ɗamara, ka sha ɗamara da shi kada kuwa ka tsoma shi a ruwa.”
2 Sai na sayo abin ɗamara kamar yadda Ubangiji ya ce, na sha ɗamara da shi.
3 Ubangiji kuma ya sāke yin magana da ni sau na biyu,
4 ya ce, “Ka ɗauki abin ɗamara da ka sayo, wanda ka ɗaura, ka tafi Kogin Yufiretis, ka ɓoye shi a cikin kogon dutse.”