8 Shi kamar itace ne wanda ake dasa abakin rafiWanda yake miƙa saiwoyinsa zuwacikin rafin,Ba zai ji tsoron rani ba,Kullum ganyensa kore ne,Ba zai damu a lokacin fari ba,Ba zai ko fasa yin 'ya'ya ba.
9 “Zuciya ta fi kome rikici,Cuta gare ta matuƙa,Wa zai san kanta?
10 Ni Ubangiji nakan bincike tunani,In gwada zuciya,Domin in sāka wa kowane mutumgwargwadon al'amuransa,Da kuma gwargwadon ayyukansa.
11 “Kamar makwarwar da ta kwantakan ƙwan da ba ita ta nasa ba,Haka yake ga wanda ya sami dukiyarharam,Yana gaɓar ƙarfinsa, za ta rabu dashi,A ƙarshe zai zama wawa.”
12 Kursiyi mai daraja,Da aka sa a bisa tun daga farko,Wurin ke nan inda Haikalinmuyake.
13 Ya Ubangiji, begen Isra'ila,Duk waɗanda suka rabu da kai, za susha kunya.Waɗanda suka ba ka baya a duniyaza a rubuta suDomin sun rabu da Ubangiji,maɓuɓɓugar ruwan rai.
14 Ubangiji, ka warkar da ni, zan kuwawarke,Ka cece ni, zan kuwa cetu,Gama kai ne abin yabona.