8 Firistoci kuma ba su ce, ‘Ina UbangijiYake?’ ba.Masanan shari'a ba su san ni ba.Masu mulki sun yi mini laifi,Annabawa sun yi annabci da sunanBa'al,Sun bi waɗansu abubuwa marasaamfani.”
9 “Domin haka, ni Ubangiji zangabatar da ku gaban shari'a,Ku da 'ya'yanku, da 'ya'yan'ya'yanku, wato jikokinku.
10 Ku haye zuwa tsibirin Kittim wajenyamma, ku gani,Ku aika zuwa Kedar wajen gabas, kuduba da kyau,A dā an taɓa yin wani abu haka?
11 Akwai wata al'umma da ta taɓasāke gumakantaKo da yake su ba kome ba ne?Amma mutanena sun sauya darajarsuda abin da ba shi da rai.
12 Sammai, ku girgiza saboda wannan,ku razana,Ku yi shiru, ni Ubangiji na faɗa.
13 Mutanena sun yi zunubi iri biyu,Sun rabu da ni, ni da nakemaɓuɓɓugar ruwan rai,Sun haƙa wa kansu tafkunan ruwa,hudaddu,Waɗanda ba za su iya ajiye ruwa ba.
14 “Isra'ila ba bawa ba ne, ba a kumahaife shi bawa ba,Amma me ya sa ya zama ganima?