15 Sun ji kunya sa'ad da suka aikataabubuwan banƙyama?Ba su ji kunya ba ko kaɗan.Ko gezau ba su yi ba,Don haka za su fāɗi tare dafāɗaɗɗu,Sa'ad da na hukunta su, za ahamɓarar da su.Ni Ubangiji na faɗa.”
16 Haka Ubangiji ya ce,“Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba,Ku nemi hanyoyin dā, inda hanyamai kyau take,Ku bi ta, don ku hutar darayukanku.Amma suka ce, ‘Ai, ba za mu bi ta ba.’
17 Na sa muku matsara cewa, in kun jian busa ƙaho ku kula!Amma suka ce, ‘Ba za mu kula ba.’
18 “Don haka, ku ji, ya ku al'ummai,Ku sani, ku taron jama'a,Don ku san abin da zai same ku.
19 Ki ji, ya ke duniya,Ga shi, ina kawo masifa a kanwannan jama'a,Sakayyar ƙulle-ƙullensu,Don ba su kula da maganata ba,Sun ƙi dokokina.
20 Da wane nufi kuke kawo mini turaredaga Sheba,Ko raken da kuke kawowa dagaƙasa mai nisa?Ba zan karɓi hadayunku na ƙonawaba,Ba kuwa zan ji daɗin sadakokinkuba.
21 Don haka, ni Ubangiji na ce,Zan sa abin tuntuɓe a gaban wannanjama'a,Za su kuwa yi tuntuɓe, su fāɗi.Iyaye tare da 'ya'yansu, damaƙwabci,Do abokansu za su lalace.”