6 Amma zuwa gaba za ku saniNi ne Allah, wanda na yi magana da ku.”
7 Me ya fi wannan kyau?A ga manzo yana zuwa ta kan duwatsu,Ɗauke da albishir mai daɗi, labarin salama.Ya yi shelar nasara, ya ce wa Sihiyona,“Allahnki sarki ne!”
8 Waɗanda suke tsaron birni suna sowa,Suna sowa tare saboda murna!Za su ga komowar Ubangiji a Sihiyona da idanunsu!
9 Ku ɓarke da sowar murna,Ku kufan Urushalima!Ubangiji ya ta'azantar da jama'arsa,Ya fanshi birninsa.
10 Ubangiji ya nuna ikonsa mai tsarki,Ya ceci jama'arsa,Dukan duniya kuwa ta gani.
11 Ku fita, ku bar BabilaKu dukanku da kuke ɗauke da keɓaɓɓen kayan Ubangiji!Kada ku taɓa abin da aka hana,Ku kiyaye kanku da tsarki,Ku fita ku bar birnin.
12 A wannan lokaci ba za ku bukaci ku fita da garaje ba,Ba za ku yi ƙoƙari ku tsere ba!Ubangiji Allah ne zai bishe ku,Ya kuma kiyaye ku ta kowane gefe.