20 Shugaban rundunar kabilar mutanen Gad Eliyasaf ne, ɗan Deyuwel.
21 Daga nan sai Kohatawa masu ɗauke da kayayyaki masu tsarki suka tashi. Kafin su isa masaukin, an riga an kafa alfarwar.
22 Tutar zangon mutanen Ifraimu ta tashi, ƙungiyoyinsu na biye. Shugaban rundunarsu Elishama ne, ɗan Ammihud.
23 Shugaban rundunar kabilar mutanen Manassa Gamaliyel ne, ɗan Fedazur.
24 Shugaban rundunar kabilar mutanen Biliyaminu Abidan ne, ɗan Gideyoni.
25 A ƙarshe sai ƙungiyar mutanen Dan da take bayan dukan zangon, ta tashi, ƙungiyoyinsu suna biye. Shugaban rundunarsu Ahiyezer ne, ɗan Ammishaddai.
26 Shugaban rundunar kabilar mutanen Ashiru Fagiyel ne, ɗan Okran.