13 “ ‘Yanzu, ku tashi ku haye rafin Zered da kanku.’ Sai kuwa muka haye.
14 Lokacin da muka tashi daga Kadesh-barneya zuwa lokacin da muka haye rafin Zered, shekara talatin da takwas ne. Duk wannan lokaci dukan waɗanda suka isa yaƙi suka murmutu kamar yadda Ubangiji ya rantse a kansu.
15 Hakika kuwa ikon Ubangiji ya buge su har suka hallaka ƙaƙaf.
16 “Sa'ad da dukan waɗanda suka isa yaƙi suka mutu,
17 sai Ubangiji ya yi mini magana, ya ce,
18 ‘Yau za ku ratsa kan iyakar ƙasar Mowab a Ar.
19 Sa'ad da ku kuka zo kusa da Ammonawa, kada ku dame su, ko ku tsokane su, gama ba zan ba ku abin mallaka daga yankin ƙasar Ammonawa ba, domin na ba da ita ta zama mallaka ga zuriya Lutu.’ ”