21 Suka sa ni kishi da abin da ba Allah ba,Suka tsokani fushina da gumakansu,Ni kuma zan sa su su yi kishi da waɗanda suke ba mutane ba.Zan tsokane su da wawanyar al'umma.
22 Gama fushina ya kama wuta,Tana ci har ƙurewar zurfin lahira.Za ta cinye duniya da dukan amfaninta,Za ta kama tussan duwatsu.
23 “ ‘Zan tula musu masifu,Zan ƙare kibauna a kansu,
24 Za su lalace saboda yunwa,Zazzaɓi mai zafi, da muguwar annoba za su cinye su.Zan aika da haƙoran namomi a kansu,Da dafin abubuwa masu jan ciki.
25 Waɗanda suke a waje, takobi zai kashe su,A cikin ɗakuna kuma tsoro,Zai hallaka saurayi da budurwa,Da mai shan mama da mai furfura.
26 Na ce, “Zan watsar da su,In sa a manta da su cikin mutane.”
27 Amma saboda gudun tsokanar maƙiyi,Kada abokan gābansu su zaci su ne suka ci nasara.Ai, ni ne na yi wannan.’