6 Haka za ku sāka wa Ubangiji,Ya ku wawaye, mutane marasa hikima?Ba shi ne Ubanku, Mahaliccinku ba,Wanda ya yi ku, ya kuma kafa ku?
7 “Ku fa tuna da kwanakin dā,Ku yi tunani a kan shekarun tsararraki,Ku tambayi mahaifanku, su za su faɗa muku,Ku tambayi dattawanku, su kuma za su faɗa muku,
8 Sa'ad da Maɗaukaki ya ba al'ummai gādonsu,Sa'ad da ya raba 'yan adam,Ya yanka wa mutane wurin zama bisa ga yawan Isra'ilawa.
9 Gama rabon Ubangiji shi ne jama'arsa,Yakubu shi ne rabon gādonsa.
10 “Ya same shi daga cikin hamada,A jeji marar amfani, inda namomi suke kuka.Ya kewaye shi, ya lura da shi,Ya kiyaye shi kamar ƙwayar idonsa.
11 Kamar gaggafar da take kaɗa fikafikanta a kan sheƙarta,Tana rufe da 'yan tsakinta,Ta buɗe fikafikanta, ta kama su,Ta ɗauke su a bisa kafaɗunta.
12 Ubangiji ne kaɗai ya bishe shi,Ba wani baƙon allah tare da shi.