5 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Zan zo wurinku domin in yi shari'a. Nan da nan zan tabbatar da laifin masu yin sihiri, da na mazinata, da na masu shaidar zur, da na masu zaluntar ma'aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu, da marayu, da baƙi, da waɗanda ba su ganin girmana.”
6 “Ni ne Ubangiji, ba na sākewa, domin haka ku zuriyar Yakubu, ba ku ƙāre ɗungum ba.
7 Ku kamar kakanninku kuke, kun bar bin dokokina, ba ku kiyaye su ba. Ku komo wurina, ni ma zan koma wurinku,” in ji Ubangiji Mai Runduna. “Amma kun ce, ‘Ƙaƙa za mu yi, mu koma gare ka?’
8 Mutum zai iya zambatar Allah? Amma ku kuna zambatata, kuna kuwa cewa, ‘Ta ƙaƙa muka zambace ka?’ A wajen al'amarin zaka da hadayu, kuke zambatata.
9 Dukanku la'antattu ne gama al'ummar duka zamba take yi mini!
10 Ku kawo dukkan zaka a ɗakin ajiyata domin abinci ya samu a cikin Haikalina. Ku gwada ni, za ku gani, zan buɗe taskokin sama in zubo muku da albarka mai yawan gaske.
11 Ba zan bar ƙwari su lalatar da amfanin gonaki ba. Kurangar inabinku za ta cika da 'ya'ya, ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.