9 Sai na umarta, suka kuwa tsarkake ɗakunan, sa'an nan na mayar da tasoshin Haikalin Allah, da hadaya ta gari, turare a ciki.
10 Na kuma iske ba a ba Lawiyawa rabonsu ba. Saboda wannan Lawiyawa da mawaƙa masu hidima suka watse zuwa gonakinsu.
11 Sai na yi wa shugabanni faɗa, na ce, “Me ya sa aka ƙi kula da Haikalin Allah?” Sa'an nan na tara Lawiyawa da mawaƙa, na sa su a wuraren aikinsu.
12 Sai dukan mutanen Yahuza suka kawo zakar hatsi, da ta ruwan inabi, da ta mai, a ɗakunan ajiya.
13 Sai na sa Shelemiya, firist, da Zadok, magatakarda, da Fedaiya daga cikin Lawiyawa su zama masu lura da ɗakunan ajiya. Na kuma sa Hanan ɗan Zakkur, jikan Mattaniya ya yi aiki tare da su, gama su amintattu ne. Aikinsu shi ne su raba wa 'yan'uwansu abin da aka kawo.
14 “Ka tuna da ni, ya Allahna, saboda wannan. Kada ka manta da ayyukan kirki da na yi a Haikalin Allah da kuma na hidimarsa.”
15 A kwanakin nan na ga mutane a Yahuza suna matse ruwan inabi, suna labta wa jakunansu buhunan hatsi, da ruwan inabi, da 'ya'yan inabi, da ɓaure, da kaya iri iri, suna kawo su cikin Urushalima a ran Asabar. Sai na yi musu faɗa a kan sayar da abinci a wannan rana.