1 “Ka ce wa 'yan'uwanka maza, ‘Ku mutanena ne,’ ka kuma ce wa 'yar'uwarka, ‘Kin sami jinƙai!’
2 Ku roƙi uwarku,Gama ita ba matata ba ce,Ni kuma ba mijinta ba ne.Ku roƙe ta ta daina karuwancinta,Ta rabu da masu rungumar mamanta.
3 In ba haka ba, sai in yi mata tsiraici,In bar ta kamar ran da aka haife ta.In maishe ta kamar jeji,In bar ta kamar busasshiyar ƙasa,In kashe ta da ƙishi.
4 Ba zan yi wa 'ya'yanta jinƙai ba,Domin su 'ya'yan karuwanci ne
5 Gama uwarsu ta yi karuwanci.Ita wadda ta haife su ta yi abin kunya.Gama ta ce, ‘Zan bi samarinaWaɗanda suke ba ni ci da sha,Da ulu, da lilin, da mai, da ruwan inabi.’