13 Zan hukunta ta saboda kwanakin idodin gunkin nan Ba'al.A kwanakin nan takan ƙona musu turare,Ta yi ado da zobe da lu'ulu'ai,Ta bi samarinta, amma ta manta da ni.”In ji Ubangiji.
14 “Don haka, ga shi, zan rarrashe ta,In kai ta cikin jeji,In ba ta magana.
15 Can zan ba ta gonar inabi,In mai da kwarin Akor, wato wahala, ƙofar bege.A can za ta amsa mini kamar a kwanakin ƙuruciyarta,Kamar lokacin da ta fito daga ƙasar Masar.
16 Ni Ubangiji na ce, a waccan ranaZa ta ce da ni,‘Mijina,’ ba za ta ƙara ce da ni Ba'al ba.
17 Zan kawar da sunayen Ba'al daga bakinta.Ba za a ƙara kiransu da sunayensu ba.
18 “A waccan rana zan yi alkawariDa namomin jeji, da tsuntsaye,Da abubuwa masu rarrafe saboda Isra'ila.Zan kuma kakkarya baka da takobi,In kuma sa yaƙi ya ƙare a ƙasar,Sa'an nan za su yi zamansu lami lafiya.
19 Zan ɗaura auren da yake cikin adalci,Da bisa kan ka'ida, da ƙauna.