1 Ya ku mutanen Isra'ila, ku ji maganar Ubangiji,Gama Ubangiji yana da shari'a da ku, ku mazaunan ƙasar.“Gama ba gaskiya, ko ƙauna,Ko sanin Ubangiji a ƙasar.
2 Akwai rantsuwa, da ƙarya, da kisankai, da sata, da zina,Da kama-karya, da zub da jini a kai a kai.
3 Saboda haka ƙasar za ta yi makoki,Dukan waɗanda yake zaune a cikinta za su yi yaushi.Namomin jeji kuma, da tsuntsaye, da kifaye za su ƙare.
4 “Duk da haka kada wani ya sa wa mutum laifi,Kada wani kuma ya tsautar.Da ku nake magana, ku firistoci.
5 Za ku yi tuntuɓe da rana,Annabi kuma zai yi tuntuɓe tare da kai da dare,Ni kuwa zan hallaka mahaifiyarku.
6 Mutanena sun lalace saboda jahilci.Tun da yake sun ƙi ilimi,Ni ma na ƙi ku da zaman firist ɗina.Tun da yake kun manta da umarnan Allahnka,Ni ma zan manta da 'ya'yanku.
7 “Yawan ƙaruwar firistoci, yawan ƙaruwar zunubi.Zan sāke darajarsu ta zama kunya.