1 Zifawa suka zo wurin Saul a Gibeya suka ce, “Ba ga Dawuda yana ɓuya a kan tudun Hakila wanda yake gaban Yeshimon ba?”
2 Saul kuwa ya tashi ya tafi jejin Zif tare da zaɓaɓɓu dubu uku (3,000) na Isra'ila don ya nemi Dawuda.
3 Ya kafa sansaninsa a kan tudun Hakila wanda yake gefen hanya, a gaban Yeshimon. Amma Dawuda ya yi zamansa a jeji. Da ya ga Saul ya bi shi cikin jejin,
4 sai ya aiki magewaya, suka tabbata lalle Saul ya zo.
5 Dawuda kuwa ya tashi ya tafi wurin da Saul ya kafa sansani. Ya kuwa ga inda Saul yake kwance, da kuma Abner ɗan Ner, sarkin yaƙin Saul. Saul ya kwanta a sansanin, sojojin suna kewaye da shi.