24 “Ku 'yan matan Isra'ila, ku yi makoki domin Saul!Ya suturta ku da mulufi mai ƙayatarwa,Ya yi muku adon lu'ulu'u da zinariya.
25 “Jarumawa sun fāɗi,An kashe su a bakin dāga.Jonatan na kwance matacce a tuddai.
26 “Na damu ƙwarai saboda kai, ɗan'uwana Jonatan,Ƙaunatacce kake a gare ni!Ƙaunarka a gare ni abar al'ajabi ce,Ta fi ƙaunar mace.
27 “Jarumawa sun fāɗi,Makamansu ba su da sauran amfani.”