1 Sai kuma Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce,
2 “Ya kai ɗan mutum, ka yi makoki domin Taya.
3 Ka ce mata, ita wadda take zaune a mashigin teku, wadda take kuma kasuwar mutanen da suke bakin teku, ni Ubangiji Allah na ce,‘Ke Taya, kin ce ke kyakkyawa ce cikakkiya!
4 Teku ta kewaye kan iyakarki,Maginanki sun ƙawata ki.