7 Na ga alfarwan Kushan suna cikin azaba,Labulen ƙasar Madayana suna rawar jiki.
8 Ya Ubangiji, ka hasala da koguna ne?Ko kuwa ka yi fushi da koguna?Ko kuwa ka hasala da teku ne,Sa'ad da ka hau dawakanka, kana bisa karusarka ta nasara?
9 Ka ja bakanka,Ka rantsar da sandunan horo.Ka rarratsa duniya da koguna.
10 Duwatsu sun gan ka, sun ƙame,Ruwaye masu hauka suka gudu.Zurfi kuma ya ta da muryarsa,Raƙuman ruwansa sun tashi.
11 Rana da wata sun tsaya cik a inda suke,A lokacin da kibanka masu haske suke wucewa fyu,Da lokacin walƙatawar hasken māshinka.
12 Ka ratsa duniya da hasala,Ka kuma tattake al'umman duniya da fushi.
13 Ka fito saboda ceton mutanenka,Saboda ceton shafaffenka kuma.Ka fasa kan mugu,Ka kware shi daga cinya zuwa wuya.