11 Saboda haka yanzu, sai ka faɗa wa jama'ar Yahuza da mazaunan Urushalima, ka ce, haka Ubangiji ya faɗa, ‘Ga shi, na shirya muku masifa, ina tsara wahalar da za ta same ku. Bari kowannenku ya koma ya bar muguwar hanyarsa, ya gyara al'amuransa da ayyukansa.’
12 Amma za su ce, ‘Wannan ba abin da za mu kula da shi ba ne, mu ra'ayinmu za mu bi, kowannenmu kuwa zai yi bisa ga nufin tattaurar muguwar zuciyarsa.’
13 “Domin haka ni Ubangiji na ce,‘Ka tambayi sauran al'umma.Wa ya taɓa jin irin wannan?Budurwa Isra'ila, ta yi mugun abuƙwarai!
14 Dusar ƙanƙara mai danshi ta taɓarabuwa da tsaunukan Lebanon?Ko ruwan rafuffuka mai sanyi na kandutse ya taɓa ƙonawa?
15 Amma mutanena sun manta da ni,Sun ƙona wa gumaka turare.Sun yi tuntuɓe a cikin al'amuransu,a hanyoyin dā,Sun bi ɓarayin hanyoyi, ba su bikarauka ba.
16 Sun mai da ƙasarsu abarbanƙyama,Abin raini har abada.Duk wanda ya wuce ta wurin zairazana ya kaɗa kansa.
17 Haka zan warwatsa suKamar yadda iskar gabas take yi, agaban abokan gābansu,Zan juya musu baya, ba za su gafuskata ba,A ranar masifarsu.’ ”