18 Domin haka ga abin da Ubangiji ya ce a kan Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza,“Ba za su yi makoki dominsa ba, kosu ce,‘Wayyo ɗan'uwanmu!’ ko, ‘Wayyo'yar'uwarmu!’Ba za su yi makoki dominsa ba, suce,‘Wayyo ubangidanmu!’ ko ‘Wayyo mai martaba!’
19 Za a binne shi kamar jaki,Za a ja shi a yar a bayan ƙofofinUrushalima.”
20 Ku haura zuwa Lebanon, ku yikuka,Ku ta da muryarku cikin Bashan,Ku yi kuka daga Abarim,Gama an hallakar da dukanƙaunatattunku.
21 Ubangiji ya yi muku magana alokacin wadatarku.Amma kun ce, “Ba za mu kasakunne ba!”Wannan shi ne halinku tun kunasamari,Don ba ku yi biyayya da muryaUbangiji ba.
22 Iska za ta kwashe shugabanninku,Za a kai ƙaunatattunku cikinbauta,Sa'an nan za ku sha kunya ku ruɗe,Saboda dukan muguntarku.
23 Ya ku mazaunan Lebanon,Waɗanda suke zaune cikin itatuwanal'ul,Irin nishin da za ku yi sa'ad da azabata same ku,Azaba ce irin ta mace mainaƙuda!
24 “Ni Ubangiji na rantse da raina, ko da Yekoniya ɗan Yehoyakim, Sarkin Yahuza, zoben hatimi ne a yatsan hannun damana, duk da haka zan kwaɓe shi,