6 A zamaninsa za a ceci Yahuza,Isra'ila kuwa za ta zauna lafiya.Sunan da za a kira shi da shi kenan,‘Ubangiji Adalcinmu.’
7 “Saboda haka, ga shi, kwanaki suna zuwa, ni Ubangiji na faɗa, sa'ad da mutane ba za su ƙara cewa, ‘Na rantse da ran Ubangiji wanda ya fito da jama'ar Isra'ila daga cikin ƙasar Masar ba,’
8 amma za su ce, ‘Na rantse da ran Ubangiji wanda ya fito da zuriyar Isra'ila daga ƙasar arewa, daga kuma dukan ƙasashen da ya warwatsa su!’ Sa'an nan za su zauna a ƙasarsu ta kansu.”
9 A kan annabawa kuwa, zuciyata takarai,Dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa,Saboda Ubangiji da kuma maganarsamai tsarki.Na zama kamar mashayi, wanda yabugu da ruwan inabi,
10 Gama ƙasar cike take da mazinata,Saboda la'ana, ƙasar za ta yimakoki,Wuraren kiwo na jeji sun bushe,Manufarsu mugunta ce,Ba su mori ƙarfinsu a inda yakamata ba.
11 “Annabi da firist, dukansu biyumarasa tsoron Allah ne,Har a cikin Haikalina na tarar damuguntarsu.”Ubangiji ya faɗa.
12 “Saboda haka hanyarsu za ta zamada santsi da duhu,Inda za a runtume su, su fāɗi.Gama zai kawo musu masifa ashekarar da za su shahukuncinsu.”Ubangiji ya faɗa.