33 Waɗanda Ubangiji ya kashe awannan rana,Za su zama daga wannan bangonduniya zuwa wancan.Ba za a yi makoki dominsu ba,Ba kuwa za a tattara gawawwakinsua binne ba.Za su zama taki ga ƙasa.
34 “Ku yi makoki, ku yi kuka, kumakiyaya,Ku yi ta birgima a cikin toka kuiyayengijin garke,Gama ranar da za a yanka ku daranar da za a warwatsa ku ta zo,Za ku fāɗi kamar zaɓaɓɓen kasko.
35 Ba mafakar da ta ragu dominmakiyaya,Iyayengijin garken ba za su tsira ba.
36 Ji kukan makiyayan,Da kukan iyayengijin garken,Gama Ubangiji yana lalatar da wurinkiwonsu.
37 Garkunan da suke zaune lafiya kuwa,an yi kaca-kaca da suSaboda zafin fushin Ubangiji.
38 Ya rabu da wurin ɓuyarsa kamarzaki,Gama ƙasarsu ta zama mararamfani,Saboda takobin Ubangiji, da kumazafin fushinsa.”