15 Gama wata murya daga Dan tafaɗa,Ta kuma yi shelar masifar da za tafito daga duwatsun Ifraimu.
16 “A faɗakar da al'ummai, yana zuwa,A faɗa wa Urushalima cewa,‘Masu kawo mata yaƙi suna zuwadaga ƙasa mai nisa,Suna yi wa biranen Yahuza ihu.
17 Za su kewaye Yahuza kamar masutsaron saura,Saboda ta tayar wa Ubangiji.’ NiUbangiji na faɗa.
18 “Al'amuranki da ayyukanki sukajawo miki wannan halaka,Tana da ɗaci kuwa,Ta soki har can cikin zuciyarki.”
19 Azaba! Ba zan iya daurewa da azababa!Zuciyata! Gabana yana faɗuwa daƙarfi,Ba zan iya yin shiru ba,Gama na ji amon ƙaho da hargowaryaƙi.
20 Bala'i a kan bala'i,Ƙasa duka ta zama kufai,An lalatar da alfarwaina, ba zato batsammani,Labulena kuwa farat ɗaya.
21 Har yaushe zan yi ta ganin tuta,In yi ta jin amon ƙaho?