11 Gama mutanen Isra'ila da mutanenYahuzaSun zama marasa aminci a gare ni.Ni Ubangiji na faɗa.”
12 Sun yi ƙarya a kan Ubangiji,Suka ce, “Ba abin da zai yi,Ba wata masifa da za ta same mu.Ba kuwa za mu ga takobi ko yunwaba.
13 Annabawa holoƙo ne kawai,Maganar ba ta cikinsu.Haka za a yi da su!”
14 Saboda haka Ubangiji Allah MaiRunduna ya ce,“Domin sun hurta wannan magana,Ga shi, zan sa maganata a bakinka tazama wuta,Waɗannan mutane kuwa su zamaitace,Wutar za ta cinye su.
15 “Ya ku mutanen Isra'ila, ga shi, inakawo mukuWata al'umma daga nesa,” in jiUbangiji,“Al'umma ce mai ƙarfin hali ta tunzamanin dā.Al'umma wadda ba ku san harshentaba,Ba za ku fahimci abin da suke faɗaba.
16 Kwarinsu kamar buɗaɗɗen kabarine,Dukansu jarumawa ne.
17 Za su cinye amfanin gonakinku daabincinku.Za su ƙare 'ya'yanku mata da maza.Za su cinye garkunanku na tumaki,da na awaki, da na shanu,Za su kuma cinye 'ya'yan inabinkuda na ɓaurenku.Za su hallaka biranenku masu kagarada takobi, waɗanda kuke fariya dasu.