1 Ubangiji ya ce,“Ga shi, zan kawo iskar ɓarna akan BabilaDa mazaunan Kaldiya.
2 Zan aika da masu casawa zuwaBabila, za su casa ta,Su bar ƙasarta kango.Za su kewaye ta a kowane sashiA wannan ranar masifa.
3 Kada ku bar maharbi ya yi harbi dabakansa,Kada kuma ya sa kayan yaƙinsa,Kada ku rage samarinta,Ku hallaka dukan sojojinta.
4 Za su fāɗi matattu a ƙasarKaldiyawa,Za a sassoke su a titunansu.”
5 Allah na Isra'ila da Yahuza,Ubangiji Mai Runduna, bai yashesu ba,Ko da yake sun yi wa Mai Tsarki naIsra'ila zunubi.
6 Ku gudu daga cikin Babila,Bari kowa ya ceci ransa,Kada a hallaka ku tare da ita,Gama a wannan lokaci Ubangiji zaisāka mata,Zai sāka mata bisa ga alhakinta.
7 Babila ta zama ƙoƙon zinariya ahannun Ubangiji,Ta sa dukan duniya ta yi maye.Ƙasashen duniya sun sha ruwaninabinta, suka haukace.