1 “Ni Ubangiji na faɗa, cewa a wancan lokaci, za a fitar da ƙasusuwa daga kaburburan sarakunan Yahuza, da na sarakansu, da na firistoci, da na annabawa, da na mazaunan Urushalima.
2 Za a shimfiɗa su a rana, da a farin wata, da a gaban dukan rundunan sama, waɗanda suka ƙaunata, suka bauta wa, waɗanda suka nemi shawararsu, suka yi musu sujada. Ba za a tattara su a binne ba, amma za su zama juji a bisa ƙasa.
3 Sauran mutanen muguwar tsaran nan waɗanda suke a wuraren da na warwatsa su, za su fi son mutuwa fiye da rayuwa. Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.”
4 “Ka faɗa musu, ka ce, ni Ubangiji nace,‘Wanda ya fāɗi ba zai sāke tashi ba?Idan wani ya kauce ba zai komo kanhanya ba?
5 Me ya sa, mutanen nan naUrushalima suke ratsewa, sukekomawa baya kullayaumin?Sun riƙe ƙarya kan-kanSun ƙi komowa.
6 Na kula sosai, na saurara,Amma ba wanda ya faɗi watamaganar kirki,Ba wanda ya taɓa barin muguntarsa,Kowa cewa yake, “Me na yi?”Kamar dokin da ya kutsa kai cikinfagen fama.
7 Ko shamuwa ta sararin sama ma, tasan lokatanta,Tattabara da tsattsewa, da gaurakasuna kiyaye lokacin komowarsu.Amma mutanena ba su san dokokinaba.