10 Kai ne ka sa teku ta ƙafe,Ka kuma shirya hanya ta ruwa,Domin waɗanda kake cetonsu su haye.
11 Su waɗanda ka fansaZa su kai Urushalima da farin ciki,Da waƙa, da sowa ta murna.Za su yi ta murna har abada,Ba sauran baƙin ciki ko ɓacin zuciya har abada.
12 Ubangiji ya ce,“Ni ne wanda yake ƙarfafa ku.Don me za ku ji tsoron mutum mai mutuwa,Wanda bai fi ciyawa tsawon rai ba?
13 Kuna mantawa da Ubangiji wanda ya halicce ku,Wanda ya shimfiɗa sammai,Ya kuma kafa harsashin ginin duniya?Don me za ku yi ta jin tsoron fushin waɗanda suke zaluntarku,Da waɗanda suke shiri su hallaka ku?Fushinsu ba zai taɓa yi muku kome ba!
14 'Yan sarƙa za su fita ba da jimawa baZa su yi tsawon rai,Su kuma sami dukan abincin da suke bukata.
15 “Ni ne Ubangiji Allahnku,Na dama tekuNa sa raƙumanta suka yi ruri.Sunana Ubangiji Mai Iko Dukka!
16 Na shimfiɗa sammai,Na kafa harsashin ginin duniya,Na ce wa Sihiyona, ‘Ku jama'ata ne!Na ba ku koyarwata,Na kuwa kiyaye ku da ikona.’ ”