22 Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki, suka ce, “Ya Allah, Allahn ruhohin 'yan adam duka, za ka yi fushi da dukan taron jama'a saboda zunubin mutum ɗaya?”
23 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
24 “Ka faɗa wa jama'a su tashi, su nisanci alfarwar Kora, da ta Datan, da ta Abiram.”
25 Musa kuwa ya tashi ya tafi wurin Datan, da Abiram Dattawan Isra'ilawa suka bi Musa.
26 Sai ya ce wa jama'ar, “Ina roƙonku, ku ƙaurace wa alfarwan waɗannan mugayen mutane, kada ku taɓa kowane abu da yake nasu, domin kada a shafe ku saboda zunubansu.”
27 Sai jama'a suka tashi daga inda Kora, da Datan, da Abiram suke zama.Datan da Abiram kuwa suka fito suka tsaya a ƙofar alfarwansu tare da matansu da 'ya'yansu, da 'yan ƙananansu.
28 Sai Musa ya ce, “Da haka za ku sani Ubangiji ne ya aiko ni, in yi waɗannan ayyuka, ba da nufin kaina na yi su ba.