35 Da albarkacinka sarakuna suke mulkin jama'arka,Sa'ad da suke ƙasashen waje, ƙasa mai dausayi ka ba su,Amma ba su juyo su bar zunubi, su bauta maka ba.
36 Ga shi, a yau mu bayi ne a ƙasar da ka ba mu,Wannan ƙasa mai dausayi wadda take ba mu abinci.
37 Amfanin ƙasa duk yana tafiya ga sarakunanDa ka ɗora su a kanmu saboda mun yi zunubi.Suna yi mana yadda suka ga dama, mu da dabbobinmu,Muna cikin baƙin ciki.”
38 “Saboda wannan duka muke yin alkawari mai ƙarfi a rubuce. Shugabanninmu kuwa, da Lawiyawanmu, da firistocinmu, suka buga hatimi, suka sa hannu.”