3 Ko da yake ni ne na koya wa Ifraimu tafiya.Na ɗauke su a hannuna,Amma ba su sani ni ne na lura da su ba.
4 Na bishe su da linzamin alheri da ragamar ƙauna,Na zama musu kamar wanda yake ɗauke musu karkiya daga muƙamuƙansu.Na sunkuya, na ciyar da su.
5 “Ba su koma ƙasar Masar ba,Amma Assuriya za ta zama sarkinsuGama sun ƙi yarda su koma wurina.
6 Takobi zai ragargaje biranensu,Zai lalatar da sandunan ƙarafan ƙofofinsu,Zai cinye su domin muguwar shawararsu.
7 Mutanena sun himmantu su rabu da ni,Ko da yake an kira su ga Ubangiji,Ba wanda ya girmama shi.
8 “Ƙaƙa zan iya rabuwa da ke, ya Ifraimu?Ƙaƙa zan miƙa ki, ya Isra'ila?Ƙaƙa zan maishe ki kamar Adma?Ƙaƙa zan yi da ke kamar Zeboyim?Zuciyata tana motsawa a cikina,Juyayina ya huru.
9 Ba zan aikata fushina mai zafi ba,Ba zan ƙara hallaka Ifraimu ba,Gama ni Allah ne, ba mutum ba,Maitsarki wanda yake tsakiyarku,Ba zan zo wurinku da hasala ba.