12 Na san irin zunuban da kuke yi,Da mugayen laifofin da kuka aikata.Kuna wulakanta mutanen kirki,Kuna cin hanci,Kuna hana a yi wa talakawa shari'aradalci a majalisa.
13 Ashe, ba abin mamaki ba ne,Da masu hankali suka kame bakinsuA waɗannan kwanaki na mugunta.
14 Ku yi ƙoƙari, ku yi nagarta, bamugunta ba,Domin ku tsira.Sa'an nan ne Ubangiji AllahMaɗaukakiZai kasance tare da ku sosai,Kamar yadda kuka ɗauka!
15 Ku ƙi mugunta, ku ƙaunacinagarta,Ku yi adalci cikin majalisaralƙalanku!Watakila Ubangiji Allah MaiRundunaZai yi wa sauran da suka ragu nawannan al'umma alheri.
16 Haka Ubangiji Allah Mai Rundunaya ce,“Za a yi kuka, a yi kururuwa atitunan birninku saboda azaba.Daga ƙauyuka za a kirawomutaneSu zo su yi makokin.Waɗanda suka mutu, tare da masumakoki da aka ijarar da su.
17 Za a yi kuka ko'ina cikin dukangonakin inabinkuGama zan zo in yi muku horo.”
18 Taku ta ƙare, ku da kuke marmarinzuwan ranan nan ta Ubangiji!Wane amfani wannan rana za ta yimuku?Rana ta baƙin ciki ce,Ba ta murna ba.